News
An ceto sama da mutum 800 a ambaliya a Hadaddiyar Daular Larabawa
DAGA Kabiru Basiru fulatan
Hukumomi a ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa sun ce tawagogin aikin agaji sun ceto fiye da mutum ɗari takwas sakamakon ambaliyar da mamakon ruwan sama ya janyo.
Kusan mutum dubu huɗu aka bai wa mafaka ta wucin-gadi a arewacin masarautun Fujairah da Sharjah.
Kotun majistre ta umarci matashi da ya share haraba bisa yunƙurin yin sata
Hukumomin Daular sun ce ruwan saman shi ne mafi ƙarfi da aka taɓa samu a Fujairah cikin shekara talatin.
A Iran ma ambaliya ta shafi ɗaruruwan ƙauyuka, lamarin da ya jawo rufe manyan hanyoyi.
Kafar yaɗa labaran ƙasar Iran din ta ce mutum goma ne suka rasa rayukansu a yankin Firouz Kooh da ke arewa maso gabashin Tehran, sannan mutum goma sha shida sun ɓata.
Masu aikin ceto na ci gaba da neman waɗanda ake sa ran suna da sauran kwana.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
