News
Mun ji sassauci bayan yanke masa hukuncin kisa – Mahaifan Hanifa
Daga kabiru basiru fulatan
Mahaifiyar Hanifa Abubakar, yarinya mai shekara biyar da malaminsu ya kashe, na so gwamnati ta gaggauta zartar wa mutumin mai suna Abdulmalik hukuncin kisa da kotu ta yanke masa.
Cikin wata hira ta musamman da BBC Hausa, Murja Sulaiman Zubair ta ce “bayan yanke hukunci na ji sassaucin wani abin kuma alhamdulillahi”.
Jirgin Emirates zai rage jigilar fasinjoji a Najeriya
Shi ma mahaifin Hanifa, Abubakar Abdulsalam, ya ce ya samu natsuwa “tun da an yanke masa hukunci daidai da abin da ya aikata”, kuma ya gode wa mutane bisa addu’o’in da suka yi musu.
Babbar kotun da ke Jihar Kano a arewacin Najeriya ta yanke wa Abdulmalik hukuncin kisa ne ta hanyar rataya bisa laifin kashe Hanifa da kuma ɗaurin shekara biyu kan laifin garkuwa da ita.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
