News
Akwai Hannun Yan Kasashen Waje A Matsalar Tsaron Najeriya—- Sabon Kwanturolar Hukumar Shige da Fice, Shiyyar Kaduna
Daga: Muslim yunus Abdullahi
Kwanturola Liman Sani Kila ya koma matsayinsa na sabon Kwanturolar Hukumar Shige da Fice ta Kasa, shiyyar jihar Kaduna.
Kwanturola Liman wanda ya koma bakin aiki a wannan makon, ya umurci jami’ai d da su ci gaba da aiki yadda ya kamata, yayin da ya yi alkawarin karfafa hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro a jihar da nufin dakile safarar mutane a jihar.
A cewarsa, lamarin ba zai kasance kamar yadda aka saba ba, inda ya kara da cewa, “a matsayina na sabon Kwanturolan hukumar shige da fice ta jihar Kaduna, zan kara hada kan kokarin da Kwanturola na baya, tare da yin aiki tare da sauran hukumomin tsaro. ”
A cewarsa, galibin hare-haren ‘yan bindiga a fadin kasar nan ‘yan kasashen waje ne ke haddasa su. Kamar yadda jaridar Daily Post ta ruwaito
Da yake zantawa da ‘yan jarida jim kadan bayan taron ranstar da shi, Kwanturola Liman ya tunatar da jami’an hukumar cewa, hukumar shige da fice a Kaduna tana da wani sashe da aka riga aka kafa a shiyyar da ke aiki da kungiyar ECOWAS ke da alhakin ba da izinin zama ga baƙi zuwa cikin jihar, kamar yadda sashe na 2 na Dokar Shige da Fice ta shekarar 2015 ya ba da dama.
Ya kara da cewa jami’an rundunar ‘yan sanda na “Operation Yaki’ na aiki da hukumar domin duba ayyukan ‘yan ci-rani a kan iyaka, a matsayin babban nauyin da ya rataya a wuyansu.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
