News
Najeriya ta bayar da tallafi ga waɗanda gobarar kasuwar Nguru ta shafa
Daga Usman Abdullahi jibirin Ngurun Yobe
Gwamnatin Najeriya ta hannun hukumar bayar da agajin gaggawa ta NEMA ta bayar da tallafin abinci da kayayyaki ga waɗanda gobarar da ta tashi a kasuwar Nguru da ke Jihar Yobe ta shafa.
A makon da ya gabata ne sama da shaguna 300 suka ƙone a kasuwar.
Kafar watsa labarai ta Channels a Najeriya ta ruwaito cewa Ministar Ma’aikatar Jinkai da Cigaban Al’umma da Kare Afkuwar Bala’i wato Sadiya Umar-Faruk ce ta miƙa kayayyakin a ranar Alhamis.
Shi ma Shugaban Majalisar Dattawa Ahmed Lawan wanda shi ne sanata mai wakiltar arewacin Yobe ya bai wa waɗanda lamarin ya shafa tallafin miliyan 10.
An yi asarar kayayyaki na miliyoyin nairori a yayin gobarar.
-
Uncategorized7 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News6 days ago
Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
-
News2 days ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
