Connect with us

News

An kammala aikin ceto a wajen rushewar gini a Kano

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAH 

 

 

 

 

 

Advertisement

An kammala aikin ceto a wajen da wani bene mai hawa uku ya rushe a kasuwar beirut da ke Jihar Kano – inda gini ya danne mutane da dama

 

Jami’an agajin gaggawa sun ce mutum daya ya mutu a baraguzan gini yayin da bakwai kuma suka samu raunuka, inda aka garzaya da su zuwa asibiti domin basu kulawa da ta dace.

Mutum hudu sun kamu da cutar kyandar biri a Katsina

Sai dai hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA, ta ce daya daga cikin wadanda suka samu raunuka ya samu karaya kuma yana asibiti ana kula da shi.

 

Advertisement

Hukumar ta NEMA ta fadawa BBC cewa ta kammala aikin ceto zuwa yanzu kuma babu sauran mutane da ke karkashin baraguzan gini.

 

Benen wanda yake dauke da shaguna da dama ba a kammala gina shi ba kafin ya rushe a jiya Talata. Ba a dai san me ya haddasa rushewar ginin ba.

 

Ana yawaita samun rushewar gine-gine a biranen Najeriya da ke janyo asarar rayuka, inda sau da dama ake dora laifin hakan a kan rashin bin ka’idojin gini da mutane basa bi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending