Connect with us

News

Gwamnonin Arewacin Najeriya na so a kafa rundunar ‘yan sandan jihohi

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAH

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Gwamnonin jihohin Arewacin Najeriya 19 da sarakunan gargajiya a yankin sun yi kira da a yi garambawul ga kundin tsarin mulki na 1999, don samar da yan sandan jihohi.

Advertisement

A cewarsu wannan ne kadai zai sa a shawo kan matsalar tsaro da yankin ke fama da ita dama kasa baki daya.

Jirgin Kasa Ya Dena Jigila Daga Nguru Zuwa Kano Saboda Rashin Gata.

Advertisement

Yankin Arewacin na Najeriya ya jima yana fama da matsalar yan fashin daji, da satar mutane don neman kudin fansa, da sauran nau’o’in ayyukan ta’addanci.

Kungiyar gwamnonin arewa ta NGF, da ta sarakunan gargajiya (NTRC) sun aminta da hakan ne bayan kammala wani taro ranar Litinin a Abuja.

Advertisement

Wannan ne karon farko da kungiyoyin biyu suka cimma matsayar samar da yan sandan jihohi a taron hadin gwuiwa.

Sai dai akwai masu fargabar cewa wasu gwamnonin jihohin kan iya amfani da yan sandan da za a samar a karkashin ikonsu, don cin zarafin abokan adawa ko kuma cimma burinsu na siyasa.

Advertisement

An dade ana kiraye-kirayen samar da yan sandan jihohi, inda masu bukatar a yi hakan ke kafa hujjar cewa rundunar yan sanda ta kasa ta yi kadan, idan aka yi la’akari da girman matsalar tsaron da kasar ke fama da ita.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending