Connect with us

News

Za mu janye yajin aiki nan ba da jimawa ba – ASUU

Published

on

MALAMAN JAMI.O.E

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

Shugaban kungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya, ASUU, Farfesa Victor Emmanuel Osodekeya ce nan ba da jimawa za su koma azuzuwa domin ci gaba da koyarwa.

Ƴan Nijeriya sun kashe dala miliyan 609.5 wajen karatu a ƙasashen waje a wata 8

Ya bayyana haka ne yayin da ya gana da kakakin majalisar wakilan Najeriya, Femi Gbajabiamila ranar Litinin.

Farfesa Osodeke ya yaba wa matakin da majalisar wakilan kasar ta dauka na shiga tsoma baki domin ganin an yi sulhu tsakanin gwamnatin tarayya da kungiyar ASUU wadda ta kwashe wata takwas tana yajin aiki.

Wani bidiyo da aka wallafa a shafin Tuwita na majalisar wakilan Najeriya ya nuna Farfesa Osodeke yana cewa sun kusa kawo karshen yajin aikin.

Advertisement

BBC

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending