News
Ma’aikatan Jinya Sun Bai Wa Gwamnati Mako Daya Ta Biya Su Hakkokinsu
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Kungiyar Manyan Ma’aikatan Asibitocin Koyarwa da Cibiyoyin Bincike (SSAUTHRIAI) ta bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adin mako guda ta biya mambobinta bashin alawus-alawus din da suke bin ta.
Sanarwar hakan na cikin bayanin da kungiyar ta fitar ta hannun mukaddashin shugabanta, Malam Kabir Mustapha da sakataren riko, Mista Joseph Ugwoke, bayan taron yini biyu da kungiyar ta gudanar.
Wani magidanci ya kashe matarsa ta hanyar lakada mata duka a Ogun Police
Kungiyar ta ce ba lallai ne mamabobinta su ci gaba da zuwa aiki ba muddin gwamnati ba ta biya su dukkan hakkokinsu a cikin mako daya ba.
Don haka ta nusar da gwamnatin bukatar da ke akwai na ta biya bukatunsu don kauce wa tilasta mata shiga yajin aiki.
Ta ce ta rubuta wa gwamnati takarda sau sa da dama don yi mata tuni, amma duk da haka gwamnatin ta yi biris.
DAILY TRUST
Ta kuma nuna damuwarta kan yadda gwamnatin ta ware likitoci ta biya su ba tare da ta biya sauran ma’aikatan ba.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
