Sports
Ciwon ciki zai hana Ronaldo haskawa a wasan sada zumuncin Najeriya da Portugal
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Dan wasan Portugal Cristiano Ronaldo ba zai haska a wasan sada zumuncin shirye-shiryen gasar cin kofin duniya da za a fafata tsakanin Najeriya da kasarsa a wannan Alhamis ɗin ba.
A cewar kocinsa Fernando Santos, ɗan wasan tun jiya bai fito atisaye ba, kuma yana bukatar hutu na ɗan wani lokaci.
An cire hotunan Ronaldo a Old Trafford, Rabiot ya ce ya yi sa’a da bai je United ba
A wannan makon ne Ronaldo mai shekara 37 ya caccaki kungiyar Manchester United a wata hira da aka yi da shi, inda ya ke nuna cewa ba ya darajar kocinsa, Erik ten Hag saboda abubuwan da yake yi masa.
Sannan ya nuna cewa United ba ta yi masa adalci ba, kuma akwai ‘yan wasan da ba sa farin cikin kasancewarsa a kungiyar.
Idan Ronaldo ya warke ana sa rai ya haska a karo na biyar a gasar cin kofin duniya, babu mamaki kuma ta karshe ga ɗan wasan.
Portugal za ta yi fafatawar farko ne da Ghana a ranar 24 ga watan Nuwamba, kafin daga bisani su haɗu da Uruguay da kuma Koriya Ta Kudu.
Ɗan wasan da kasarsa Portugal ba su taɓa lashe kofin duniya ba, amma sun taka rawar gani a gasar cin kofin Turai ta 2016 da kuma lashe League a 2019.
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News7 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
