Connect with us

News

Yan Sanda Sun Kashe ’Yan Bindiga 7 A Neja

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

 

’Yan sandan sun kashe ’yan bindiga bakwai a kauyen Kumbashi da ke Karamar Hukumar Mariga ta Jihar Neja.

Advertisement

 

Mista Ogundele Ayodeji, kwamishinan ‘yan sandan jihar ne, ya tabbatar da hakan ga Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ranar Alhamis a Minna, babban birnin jihar.

Advertisement

Dan Najeriya ya zama kocin tawagar ‘yan wasan kwallon Amurka

 

“Mun samu rahoton harin da ‘yan bindigar suka kai kauyen Kumbashi, kuma nan take muka tattara jami’anmu domin daukar matakan tsaro cikin gaggawa,” in ji shi.

Advertisement

 

Ya ce rundunar ‘yan sanda da ‘yan banga da ke zaune a garin Kumbashi sun yi artabu da ‘yan bindigar, inda suka kashe bakwai daga cikin maharan yayin da wasu suka tsere.

Advertisement

 

Ayodeji ya bayyana cewar wasu daga cikin ‘yan banga sun samu raunuka kuma an kai su Babban Asibitin Kontagora domin ba su kulawa.

Advertisement

 

Kazalika, rundunar ‘yan sandan ta kama wasu bata gari 17 da ake zarginsu da aikata laifuka a sassa daban-daban na kananan hukumomin Chanchaga da Bosso na jihar.

Advertisement

 

Ya ce, a ranar 5 ga watan Nuwamba, 2022 wasu bata gari da ke kewayen Angwan-Daji da Limawa, sun yi artabu da muggan makamai, kuma a sakamakon haka aka kashe wani Ashiru Tofa mazaunin yankin Limawa.

Advertisement

 

Ayodeji ya ce, rundunar ‘yan sandan, ta samu nasarar cafke wasu mutane 17 da ake zargin ‘yan ta’adda ne a yankin Angwan-Daji da kuma Limawa.

Advertisement

 

Ya yi bayanin cewa, ‘yan sanda sun kama wani kasurgumin mai kwacen wayar hannu a yankin Limawa, wanda yake basaja a matsayin mai hawa babur mai kafa uku domin yi wa wadanda abin ya shafa fashin waya.

Advertisement

 

Ayodeji ya ce wanda ake zargin ya taimaka wa ‘yan sanda wajen kama wasu bata-gari guda 17 a sassa daban-daban na birnin.

Advertisement

 

“Abubuwan da aka gano a hannun wadanda ake zargin sun hada da almakashi guda uku, tukwanen tabar shisha guda biyu da kwalaben maganin tari guda bakwai da kuma fakitin sigari,” in ji shi.

Advertisement

 

Ya ce da zarar sun kammala bincike za a gurfanar da duk wadanda ake zargin a gaban kuliya.

Advertisement

 

Kwamishinan ‘yan sandan ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ganin an yi maganin duk wasu da ake zargi da aikata miyagun laifuka kamar yadda doka ta tanada.

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending