News
NNPP: ‘Ba za mu sa hannu kan shirin zaman lafiya lokacin zabe a Kano ba’
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Jam’iyyar adawa ta NNPP da ɗan takararta na gwamna a jihar Kano dake arewa maso yammacin Najeriya, sun yi barazanar ƙauracewa sa hannu a yarjejeniyar zaman lafiya don tabbatar da ganin an gudanar zaɓuka cikin kwanciyar hankali da lumana.
Gwamnatin jihar Kano ta haramta wa Yan Adaidaita Sahun bin manyan Titunan jihar Kano
Shugaban jam’iyyar a Kano, Alhaji Umar Haruna Doguwa, ya shaida wa BBC cewa, su a tsarinsu ba zasu je su sanya hannu a kan abin da suka san cewa idan aka tabasu ba zasu kyale ba.
Ya ce, an yi irin haka ba sau daya ba to a yanzu sun kai makura.
Shugaban na NNPP a Kano, ya ce ko baya bayan nan shugaban APCn, Abdullahi Abbas sai da ya ce koda tsiya-tsiyar sai sun ci zabe.
Advertisements
