News
NNPP: ‘Ba za mu sa hannu kan shirin zaman lafiya lokacin zabe a Kano ba’
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Jam’iyyar adawa ta NNPP da ɗan takararta na gwamna a jihar Kano dake arewa maso yammacin Najeriya, sun yi barazanar ƙauracewa sa hannu a yarjejeniyar zaman lafiya don tabbatar da ganin an gudanar zaɓuka cikin kwanciyar hankali da lumana.
Gwamnatin jihar Kano ta haramta wa Yan Adaidaita Sahun bin manyan Titunan jihar Kano
Shugaban jam’iyyar a Kano, Alhaji Umar Haruna Doguwa, ya shaida wa BBC cewa, su a tsarinsu ba zasu je su sanya hannu a kan abin da suka san cewa idan aka tabasu ba zasu kyale ba.
Ya ce, an yi irin haka ba sau daya ba to a yanzu sun kai makura.
Shugaban na NNPP a Kano, ya ce ko baya bayan nan shugaban APCn, Abdullahi Abbas sai da ya ce koda tsiya-tsiyar sai sun ci zabe.
-
Uncategorized7 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News6 days ago
Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
-
News2 days ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
