News
An saki wanda ya kashe jarumin da ya yaƙi wariyar launin fata a Afrika ta Kudu
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Ma’aikatar shari’a ta Afirka ta Kudu ta tabbatar cewa an saki mutumin da ya kashe Chris Hani, jarumin da ya yi yaƙi da wariyar launin fata a ƙasar.
Matakin da Kotun Tsarin Mulkin ta ɗauka a watan da ya gabata na sakin Janusz Walus ya janyo cece-kuce da suka a Afirka ta Kudu.
Matar Mista Hani ta yi kakkausar suka kan matakin. A dai shekarar 1993 ne aka harbe Mista Hani.
Kisan na shi wani yunƙuri ne da bai yi nasara ba na miƙa mulki hannun farar hula daga mulkin tsirarun farar fata.
BBC ta rawaito cewa A makon da ya gabata ne, Mista Walus ya samu kulawar likitoci a gidan yari bayan da wani fursuna ya daɓa masa wuƙa.
Advertisements
