News
An umurci mutane su zauna cikin shirin ko-ta-kwana bayan aman dusten Lascar
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Jami’ai a Chile sun gargadi mutane da su zauna cikin shirin ko-ta-kwana bayan da dutsen Lascar ya yi aman hayaki zuwa sararin samaniya.
Dutsen na Lascar dai ke a Andes, ya fara aman hayaki ne jiya Asabar, wanda ya janyo barazanar girgizar ƙasa.
Ba a dai samu asara ba a yankin kawo yanzu, amma an sanya alamun gargadi.
BBC ta rawaito cewa Hukumar kula da harkar ma’adinai da duwatsu, ya ce alamar gargadin na nuna cewa akwai matsala a yankin.
Sai dai, jami’ai na can suna sanya ido domin kare mutane kan barazanar samun fashewa ko tashin hayaki.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
