Connect with us

News

Gobara: An Yi Asarar Rayuka 166 A Kano A Shekarar 2022

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD

 

 

Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta ce mutum 166 ne suka rasu, sannan kuma an yi asarar dukiya ta Naira miliyan 358 da ta kone a shekarar 2022 da muka yi bankwana da ita.

 

Kakakin hukumar, Saminu Yusuf Abdullahi ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin.

Advertisement

 

Buhari zai sanya hannu kan kasafin kuɗin 2023′

Ya bayyana cewa mutum 1,035 da dukiyar da ta kai kwatankwacin Naira miliyan 905 suka ceto a shekarar.

 

“Mun samu kiraye-kirayen gaggawa 736, da kuma wasu na jabu 208 a 2022.

 

 

Advertisement

“Mun kai dauki wurare 575 da aka samu hatsari a jihar, sai kuma dabbobi 6 da su ma muka ceto su a shekarar.

 

Abdullahi ya kuma ce da dama daga gobarar da aka samu a shekarar sanadiyyar iskar gas ce, da kuma amfani da kayayyakin lantarki marasa inganci.

 

Ya shawarci al’umma a wannan lokaci na sanyi, da su tabbatar sun kashe wutar jin dumi da wadataccen ruwa, gudun tashin gobarar.

 

Advertisement

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending