Connect with us

News

KANO:Kotu ta bada umarnin a kamo dan mai unguwa bisa zargin fasa idon wata amarya

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Kotun majistare mai namba 25 wadda mai shari’a Halima Wali ke jagoranta ta umarci mai binciken laifuka na ofishin ‘yan sanda da ke Zango a yankin karamar hukumar Ungogo ya gabatar da wani Ibrahim Kwajalawa cikin sa’o’I 24.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Tun farko dai an zargi wasu mutane da laifin fasawa wata amarya Khadija Abdullahi ido yayin bikinta a makon jiya, inda bayan al’amarin ya faru ne ‘yan sanda suka gurfanar da wasu mutane biyu da suka hada da Yahya Adamu, da Salisu Adamu a gaban kotu bisa zargin hada kai da raunata amaryar wanda hakan ya sa ta rasa idota guda daya.

 

Advertisement

JAPAN: Za a rufe kamfanin mujallar da ta kwashe shekaru 100 

 

 

Advertisement

Daya daga cikin ‘yan uwan amarya ta shaidawa kotun cewa, akwai dan gidan mai Unguwar cikin wadanda ake zargi, amma jami’an ‘yan sanda sun sallame shi, duk da cewa shi ake zargi da jagorantar matasan da suka aikata lefin.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Maishari’a Halima Wali, ta umarci ‘yan sanda su kawo dan mai unguwar cikin nan da awa 24 domin yi wa kowa adalci.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Kotun ta aike da sauran mutane biyun zuwa gidan ajiya da gyaran hali, har zuwa lokacin da za a dawo kotun domin ci gaba da sauraron shariar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending