Connect with us

News

An Guntule Kan Shugaban Karamar Hukuma A Imo 

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Kasa da awa 48 bayan an sace Kantoman Karamar Hukumar Ideato ta Arewa da ke jihar Imo, Chris Ohiu, an tsinci gawarsa ba kai.

Advertisement

 

Wakilinmu ya rawaito cewa an guntule kan nasa ne ranar Lahadi, bayan wasu ’yan bindiga sun sace shi.

Advertisement

Bayanai sun nuna cewa an sare kan nasa ne bayan an karbi kudin fansar Naira miliyan shida.

Za a Fuskanci Matsala Matukar Gwamnati Ta Hana Shigo Da Takin Zamani 

An dai sace Chris ne tare da wasu mutum biyu ranar Juma’a a kauyensu da ke Imoko a yankin Arondizuogu. Maharan sun kuma farmaki ilahirin kauyen nasa.

Advertisement

 

 

Advertisement

An ce maharan dai sai da suka harbi mutumin a ka kafin su yi awon gaba da shi.

 

Advertisement

Wakilinmu ya ga wani bidiyon Kantoman yana durkushe da gwiwoyinsa a kasa, yayin da masu garkuwar da shi suke gargadin Gwamnan Jihar, Hope Uzodinma cewa shi ma hakan za ta faru da shi nan ba da jimawa ba.

 

Advertisement

Bayan sun hallaka Kantoman ranar Lahadi, sun kuma wallafa bidiyonsa ta hanyar amfani da wayarsa a ‘status’ din Whatsapp dinsa.

 

Advertisement

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar, SP Henry Okoye, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ya ce tuni jami’ansu sun dukufa bincike a kan lamarin.

 

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending