Connect with us

News

An Kashe Mutum Daya A Taron APC A Jigawa

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN  

 

Advertisement

An kashe wani mutum a wajen gangamin yakin neman zaben jam’iyyar APC a Karamar Hukumar Kazaure ta Jihar Jigawa.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Emmanuel Ekot, ya shaida wa manema labarai cewa, jami’ansa na bin diddigin wanda ake zargi da kisan wanda tuni ya tsere zuwa Jihar Kano.

Advertisement

A ƙarshe, Ganduje ya kori Muhuyi Magaji

“’Yan sanda suna bincike a kan lamarin. Wanda ake zargin ya gudu Kano. Rikici ne tsakanin magoya bayan jam’iyya mai aminci da wani dan takara.

“Magoya bayan duk na APC ne. Ba rikici ne tsakanin bangarori biyu ba,” in ji Kwamishinan.

Advertisement

Gwamnan Jihar Jigawa, Muhammad Abubakar Badaru, ya jagoranci gangamin yakin neman zaben gwamna na jam’iyyar APC da aka gudanar a garin Kazaure a ranar Talata, inda rikici ya barke tsakanin kungiyoyin matasan magoya bayan jam’iyyar APC da ya yi sanadin mutuwar mutum daya.

Mutumin da aka kashe dai mai goyon bayan dan takarar kujerar Sanatan jam’iyyar ne a shiyyar Jigawa ta Arewa Maso Yamma, Babangida Husseini.

Advertisement

Mazauna garin sun bayyana cewa marigayin Halliru Lafka mazaunin garin Kazaure ne.

Kisan ya haifar da zanga-zanga a tsakanin mazauna garin inda suka rika kona duk wani allo mai dauke da hotunan Husseini.

Advertisement

Masu boren na zarge dan takarar da daukar nauyin ‘yan bangar siyasa wanda ya haifar da tarzoma a garin.

Sai dai Aminiya ta gaza jin ta bakin Hussaini kan lamarin, sakamakon wayarsa na kashe har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Advertisement
Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending