Connect with us

News

Zazzabin Lassa Ya Bulla A Gombe

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

 

Wasu rahotanni daga Jihar Gombe sun bayyana cewar an samu bullar cutar zazzabin Lassa a jihar.

 

Kwamishinan Lafiya na jihar, Dokta Habu Dahiru wanda ya bayyana hakan a ranar Laraba ya ce an gano wata mata dauke da cutar.

Advertisement

An Kashe Mutum Daya A Taron APC A Jigawa

 

“Lokacin da ta ke dawowa Gombe sai ta fara zazzabi sannan aka kwantar da ita a Asibitin Koyarwa na Gwamnatin Tarayya da ke Gombe.

 

“Bayan fitowar sakamakon gwajin da ta aka yi mata an tabbatar tana dauke da zazzabin Lassa.

 

 

Advertisement

“An kafa tawagar bayar da agajin gaggawa na jiha tare da samar da magunguna don hana yaduwar cutar,” in ji shi.

 

Ya kara da cewa gwamnatin jihar ta samar da dakin gwaje-gwaje da kuma wajen killace masu dauke da cutar.

 

“Mun kuma kafa cibiyar kebe masu cutar a shiyoyi uku na jihar a matsayin wani mataki ka dakile cutar,” in ji shi.

 

Advertisement

Kwamishinan ya kara da cewa, Kwamitin da aka kafa zai ci gaba da zagaye domin gano wadanda suka kamu da cutar tare da wayar da kan jama’a kan alamun zazzabin Lassa.

 

 

“Samun mutum daya dauke da zazzabin Lassa, na nufin annoba ta barke,” in ji Dahiru.

 

Ya yi kira da a rika tsaftace muhalli don dakile yaduwar cutar zazzabin Lassa a Jihar Gombe.

Advertisement

 

“Tsaftar jiki da ta muhalli da kuma tabbatar da kiyaye matakan kariya daga cutar Lassa,” in ji Dahiru.

 

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending