Connect with us

News

Buhari ya toge kan zuwa Kano.

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

Duk da janye gayyatar da gwamnatin Kano ta yi wa shugaban kasa Muhammadu Buhari domin bude wasu ayyuka da ta yi, da alama shugaban na nan tafe a ranar Litinin.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

A wani sako mai harshen damo da mataimakin shugaban kan kafafen sada zumunta, Bashir Ahmad ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya tabbatar da cewa Buhari na tafe a gobe Litinin.

Advertisement

 

Illar Amfani Da Manhajar Stark (VPN) ta   Kyauta

 

Advertisement

 

Har ila yau, a wani sakon na daban, Bashir Ahmad yace duk wani mai shirin jifan shugaba Buhari a jihar Kano, to babu hannun Kanawa a ciki.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Da fari dai, gwamnatin Kano ta janye gayyatar da ta yi wa shugaban ne, biyo bayan jifan da tawagarsa ta sha a jihar Katsina.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Hakan dai ba zai rasa nasaba da batun sauyin takardun naira 200, 500 da kuma 1000 da gwamnatinsa ta toge akan sai ya tabbata ba.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Yanzu haka kwanaki 2 suka rage wa’adin dena karbar tsaffin takardun ya cika, wanda hakan ke nufin ga duk wanda bai sauya kudinsa ba, to zai tafka asara.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Lamarin a yanzu, ya haddasa tsayawar kasuwanci cak a wasu kasuwannin, sabida dakatar da tsaffin takardun da tuni wasu yan kasuwa suka yi, gabanin cikar wa’adin da babban bankin kasar CBN ya bayar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending