News
Shugaban Tunisia na kama ‘yan jarida da masu hamayya da gwamnatinsa
‘Yan sanda a Tunisia sun kama shugaban wani gidan rediyo a rana ta uku na kamen ‘yan siyasa da masu fafutika.
Wakiliyar BBC ta ce, Mahukunta sun kai sumame gidan Noureddine Boutar, na tashar Mosaique FM, da ke yawaita watsa shirye-shirye da ke caccakar shugaban kasar Kais Saied.
Tun ranar Asabar, ‘yan sanda suka kama wani hamshakin ɗan kasuwa, Kamal Eltaief, da fitaccen ɗan siyasa, Khayam Turki, da wani jigo a jam’iyyar hamayya, da wasu alkalai biyu da tsohon jami’in diflomasiyya.
Yayin da ake nuna damuwa kan ‘yancin siyasa, Shugaba Kais Saied ya kare matakinsa, da ya ce ya yi daidai da doka, kuma hakan yana da amfani domin kare Tunisia daga faɗawa cikin rikici.
Advertisements
