Connect with us

News

Ruwan Sama Ya Lalata Gida 105 A Ekiti

Published

on

 

Ruwan sama kamar da bakin kwarya ya yi sanadin lalacewar gidaje akalla 105 a yankin Oke-Ako da ke Karamar Hukumar Ikole ta Jihar Ekiti.

Advertisement

 

Haka kuma ya lalata cibiyoyin wutar lantarki a fadin garin, lamarin da ya jefa mutanen cikin duhu.

Advertisement

 

Akalla sojoji tara ne suka mutu a harin kunar bakin wake a Pakistan

Gwamnan Jihar Ekiti, Biodun Oyebanji, yace a lokacin da yake tantance asarar da aka yi a garin a ranar Lahadi, ya jajanta wa mazauna garin.

Advertisement

 

Oyebanji, wanda ya samu wakilcin mataimakiyarsa, Misis Monisade Afuye, ta bayyana faruwar lamarin a matsayin mummunar barna.

Advertisement

 

Sarkin garin Ogunbiyi Tinuade Adebayo, ya gudanar da zagayen yankunan da lamarin ya shafa.

Advertisement

 

Dan majalisa mai wakiltar mazabar Ikole ta 2, Adeoye Aribasoye da Shugaban Karamar Hukumar Ajoni, Michael Ogungbemi su sun ziyarci yankunan don jajanta musu.

Advertisement

 

“Gwamnati ta damu da halin da aka tsinci kai a ciki, amma ina tabbatar muku da cewar za a tallafa muku.

Advertisement

 

“Za mu ba da duk wani goyon bayan da ya dace don dakile duk wani tasiri da wannan lamarin ya haifar ga rayuwarku,” in ji mataimakiyar gwamnan.

Advertisement

 

 

Advertisement

Aribasoye ya tabbatar wa jama’a cewa nan ba da dadewa ba za a kawo dauki ga wadanda abin ya shafa.

 

Advertisement

Ya bukace su da su kwantar da hankalinsu don bai wa gwamnati hadin kai domin su taimakawa wajen rage musu radadin halin da suke ciki.

 

Advertisement

Babban Daraktan Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Ekiti, Mista Jide Borode, ya ce za a iya rage tasirin ruwan sama, idan mutane suka rungumi shirin dasa itatuwa na gwamnatin jihar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending