Connect with us

News

Ƴan bindiga sun kashe  da mace mai ciki   a jihar Naija.

Published

on

 

 

Advertisement

Ƴan ta’adda sun hallaka wata mata mai juna biyu na wata shida da wasu mutum huɗu a garin Agwa da ke ƙaramar hukumar Rafi ta jihar Naija.

 

Advertisement

Haka kuma ‘yan ta’addar sun sace kusan mutum 50 da raunata wasu a hare-haren da suka kai jiya Talata a yankin ƙaramar hukumar ta Rafi da kuma Wushishi kamar yadda jaridar Vanguard.

Mun Shirya Samar Da Tsaro A Kano —’Yan Sanda

Rahotanni sun ce maharan sun riƙa harbin kan mai-uwa-da-wabi a lokacin da suka kai farmakin, sai dai sojoji sun katse musu hanzari inda suka farmake su da hari ta sama.

Advertisement

 

Duk da cewa sojojin sun kore su to amma ƴan bindigar sun yi awon-gaba da mutum aƙalla 50, yawanci yara da mata kamar yadda bayanai suka nuna.

Advertisement

 

Al’ummar yankin da abin ya faru na nuna fargaba kan tsaronsu yayin da ake shirin zaɓen gwamna da ƴan majalisar dokokin jiha ranar Asabar.

Advertisement

 

Kwamishinan tsaro da ayyukan jin-ƙai na jihar, Emmanuel Umar, wanda ya tabbatar da kai harin zuwa lokacin bayyana labarin, ya ce ba su tantance yawan mutanen da lamarin ya rutsa da su ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending