Connect with us

News

An sanya dokar hana fita a wani yankin Kaduna

Published

on

 

Gwamnatin jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya ta sanya dokar hana fita ta s’o’i 24 a unguwannin Sabon Garin Nassarawa da Tirkaniya a yankin ƙaramar hukumar Chikun.

Advertisement

 

A wata sanarwa da kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida na jihar Samuel Aruwan ya fitar, ya ce an ɗauki matakin ne bayan wani rikici na ‘yan sara-suka da ya kaure, da ya yi sanadin mutuwar mutum biyu.

Advertisement

Wani Dan Sanda Ya Mutu Yana Kokarin Raba Fada A Neja

Sanarwar ta kuma umarci jami’an tsaro da su tabbatar da dokar a unguwar, domin maido da zaman lafiya, yayin da ake ci gaba da bincike domin gano musabbabin abin da ya haddasa hargitsin.

 

Advertisement

A domin haka ne kwamishinan ya yi kira ga mazauna yankin da su yi biyayya ga dokar hana fitar, wadda ta fara aiki nan take.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending