Connect with us

News

An sanya dokar hana fita a wani yankin Kaduna

Published

on

 

Gwamnatin jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya ta sanya dokar hana fita ta s’o’i 24 a unguwannin Sabon Garin Nassarawa da Tirkaniya a yankin ƙaramar hukumar Chikun.

 

A wata sanarwa da kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida na jihar Samuel Aruwan ya fitar, ya ce an ɗauki matakin ne bayan wani rikici na ‘yan sara-suka da ya kaure, da ya yi sanadin mutuwar mutum biyu.

Wani Dan Sanda Ya Mutu Yana Kokarin Raba Fada A Neja

Sanarwar ta kuma umarci jami’an tsaro da su tabbatar da dokar a unguwar, domin maido da zaman lafiya, yayin da ake ci gaba da bincike domin gano musabbabin abin da ya haddasa hargitsin.

 

Advertisement

A domin haka ne kwamishinan ya yi kira ga mazauna yankin da su yi biyayya ga dokar hana fitar, wadda ta fara aiki nan take.

 

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending