Connect with us

News

Rikicin Shugabanci Ya Kunno Kai A Majalissar Dokokin Jihar Nasarawa

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

 

An samu bayyanar wakilai biyu dake ikirarin samun kujerar jagorantar majalisar dokoki ta 7 a jihar Nasarawa.

Advertisement

Ibrahim Balarabe da Daniel Ogazi dukkansu daga shiyyar yammacin jihar sune wakilan biyu dake ikirarin shugabancin kuma dukkansu ‘yan APC ne.

INEC Ta Amince Da Sunayen ‘Yan Takarar Gwamna A Jahohin Bayelsa, Kogi Da Imo.

A jiya Talata 6 ga watan Yuni ne aka shirya kaddamar da majaliisar ta 7 da kuma zaben kakakin majalisar da mataimakinsa amma magatakardan majalissar ya sanar da dage zaben saboda dalilan tsaro.

Advertisement

Daga karshe mambobi 11 ne suka zabi Ibrahim Balarabe da Jacob Kudu a matsayin kakakin majalisa da mataimakinsa a daya daga cikin ma’aikatun jihar inda mukaddashin magatakardar majalisar Ibrahim Musa ya rantsar da su.

Amma an zabi Ogazi da Adamu Oyanki a matsayin kakakin majalisa da mataimakinsa da wakilai 13 a harabar majalisar.

Advertisement

Bayan haka Gwamna Abdullahi Sule ya karbi bakuncin Balarabe da Kudu da sauran ‘yan tsaginsa a fadar gwamnatin jihar Nasarawa da ke birnin Lafiya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending