News
Hukumar Karota zata Sauyawa Jami’anta Kaki
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.
Sabon shugaban Hukumar Kula da zirga zirgar ababen hawa ta jihar Kano da aka fi sani da KAROTA, Injiniya Faisal Mahmud Kabir ya ce , za’a yiwa jami’an Hukumar sabon Kaki da kuma yin garan bawul kan yadda ake gudanar da aiyukan hukumar.
Shugaban ya baiyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin jami’an karota na musamman dake aikin sa kai a ofishinsa, a wata ziyarar bangirma da suka kai masa.
Bayanin hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin hukumar Nabilusi Abubakar Ya fitar a jiya.
Shugaban hukumar Karotar ya tabbatar da cewar zasu yi duk abunda ya dace bisa hurumin da suke dashi a dokance, domin kula da zirga-zirgar ababen hawa da kuma tsaftace yadda ake amfani da titinan jihar kano.
Advertisements
