Connect with us

News

Shariar Gwamnan Kano: Gwamna Abba Kabir Ya ya garzaya Gaban Kotun Daukaka Kara

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

To yanzu haka dai a hukumance, Gwamna Abba Kabir Yusuf na nan jahar Kano ya garzaya gaban kotun daukaka kara domin kalubalantar hukuncin da kotun sauraren kararrakin zaben gwamna ta yanke na sauke shi daga kan kujerarsa ta gwamnan kano.

 

Advertisement

Gwamnan ya gabatar da wasu hujjoji har guda 23 a gaban kotun daukaka karar, wanda yake fatan zata yi amfani dasu domin soke hukuncin da kotun kararrakin zaben gwamnan kano ta yanke.

Attajiri Ya Tausayawa Mutane a Kano, An Saida Fetur a Kan N415 a Maimakon N615

Ya baiyana cewar kotun ta yi abunda ya sabawa doka, a lokacin da ta dogara da sashi na 71 da kuma 63 na dokar zabe ta kasa wajen soke kuri’u dubu 165 da 616 daga cikin kuri’un da aka zabe shi da su.

Advertisement

 

A cikin kunshin karar mai shafuka 35, da gwamnan kano da kuma jam’iyyar sa ta NNPP suka daukaka, sun bukaci kotun daukaka karar data tabbatar dashi a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan kano na ranar 18 ga watan Maris din bana.

Advertisement

Wani labarin kuma Attajiri Ya Tausayawa Mutane a Kano, An Saida Fetur a Kan N415 a Maimakon N615

 

Advertisement

A yayin da ake cigaba da samun cikas wajen balaguro a filin jirgin sama na Murtala Muhammed dake Legas, biyo bayan komawar da kamfanonin jiragen sama na kasashen waje suka yi zuwa sabuwar tashar jiragen sama, gwamnatin tarayya ta gayyaci kamfanonin jiragen sama na kasashen waje zuwa wani taro a yau.

 

Advertisement

A sakamakon haka, kwamitin da ministan harkokin sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ya kafa domin duba rudanin tafiye-tafiye a filin jirgin sama naMurtala Muhammad da kwamitin ministoci zai gana da masu ruwa da tsaki a domin nemo bakin zaren da warware matsalar.

 

Advertisement

Fasinjojin kasa da kasa da suka tashi daga Najeriya a ranakun Laraba da Alhamis sun makale a biranen Legas da Cairo da Doha da Landan, da sauran wurare bayan da madaurin kaya na jirgi ya lalace a sabon filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas, al’amarin da ya tilastawa kamfanonin jiragen sama jinkirtawa tare da soke tashin jirage.

 

Advertisement

Har yanzu zuwa karshen mako matsalar tafiye-tafiye na ci gaba da wanzuwa inda fasinjojin ke kwashe sa’o’i a kan layi domin tantance su ta hanyar binciken tsaro

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending