News
Yan bindiga sun halaka wasu jami’an sintiri guda 9 a jihar Bauchi.
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Yan bindiga sun halaka wasu jami’an sintiri guda tara da aka fi sani da Yan Ba Beli a jihar Bauchi.
Lamarin ya faru ne a kauyen Gamji lokacin da jami’an sintirin ke farautar ‘yan bindigar da suka addabi garuruwan Karamar hukumar Ningi.
Rahotanni sun baiyana cewar yan bindigar sun yiwa jami’an sintirin kwantan bauna tare da halaka guda tara daga cikinsu a nan take, yayin da wasu kuma suka ji ciwuka.
Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ta karyata rade-radin da ke nuna shakku kan allurar cutar mashako
Daya daga cikin ‘yan kungiyar sintirin da ya bukaci a sakaye sunansa, ya fadawa manema Labarai cewar lamarin ya faru ne da yammacin ranar Lahadin data gabata a lokacin Jami’an Sintirin ke shiga tsaunikan dake kauyen Gamji domin neman yan bindigar.
A wani labarin kuma Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ta karyata rade-radin da ke nuna shakku kan allurar cutar mashako
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News2 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
