Connect with us

News

Rundunar Yan Sanda A Jihar Imo Sun Gargadi Masu Shirin Kawo Cikas Ga Zaben Gwamna Dake Tafe

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

Rundunar ‘yan sandan jihar Imo ta gargadi kungiyoyin kwadago da su guji tursasa masu kada kuri’a a zaben da za a gudanar a ranar Asabar a jihar, tana mai cewa ba za ta zuba idanu akan duk wani shiri na kawo cikas ga zaben.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Henry Okoye, ya ce an jibge ‘yan sanda sosai a fadin jihar bayan tantance yanayin tsaro.

Zamu  Cigaba Da Amfani Da Tsaffin Takardun Kudi Na Naira  – CBN

Da yake magana kan yajin aikin kungiyar kwadago, Okoye ya dage cewa kungiyoyin kwadago ba su da ikon da tsarin mulki ya ba su na dakatar da zabe, don haka ya gargadi shugabannin kungiyoyin da su guji tursasa masu zabe.

Dangane da barazanar kungiyar IPOB da kungiyar tsaro ta Gabas, kakakin ‘yan sandan ya ce rundunar ‘yan sandan za ta yi maganin duk wani mutum ko kungiyar da ke da ra’ayin aikata laifuka da nufin  kawo cikas a zaben.

A wani labarin kuma Zamu  Cigaba Da Amfani Da Tsaffin Takardun Kudi Na Naira  – CBN

Advertisement

Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.

Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.

A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.

Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending