News
Zaben Gwamnan Jahar Kogi: Jam’iyyun Siyasa Sun Amince Da Yarjejeniyar Zaman Lafiya
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gabanin zaben gwamnan jihar Kogi a ranar Asabar, jam’iyyun siyasa goma sha takwas da zasu fafata a zaben sun sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya.
Da yake jawabi a wajen taron, shugaban kwamitin zaman lafiya na kasa, Janar Abdulsalam Abubakar mai ritaya, ya ja hankalin ‘yan takarar gwamna a jihar.
Sojojin Isra’ila da mayakan Hamas suna fafatawa a kan titunan Gaza
Abubakar, wanda John Onaiyekan ya wakilta, ya ce ya fara nuna shakku sosai a kan jajircewar ‘yan takarar da ke cikin irin wannan yarjejeniyar zaman lafiya wajen biyayya ga alkawarin.
Sai dai ya bukaci jam’iyyun da su tabbatar sun yi biyayya ga yarjejeniyar a lokacin zabe.
A wani labarin kuma Sojojin Isra’ila da mayakan Hamas suna fafatawa a kan titunan Gaza
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
