News
Wata gobara ta tashi a babbar kasuwar Gamboru da ke Maiduguri
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wata gobara ta tashi a babbar kasuwar Gamboru da ke Maiduguri babban birnin jihar Borno da sanyin safiyar Lahadi.
Daily Post ta rawaito cewa Har yanzu dai ba a gano musabbabin barkewar gobarar ba. Rahotanni sun ce an dauki kokarin kungiyoyin ‘yan banga da suka hada da Civilian JTF da mazauna yankin wajen kashe wutar.
Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Borno, SEMA, ta tabbatar da faruwar lamarin a shafinta na Facebook a lokacin da babban daraktan hukumar Dr Barkindo Muhammad Saidu ya ziyarci inda lamarin ya faru a safiyar yau.
“Gobarar da ta tashi da sanyin safiyar ranar Lahadi 12/11/2023 ta kone shaguna, duk da cewa ba a tantance hasarar rayuka ba,” in ji hukumar.
Gobarar dai ta zo ne watanni tara bayan da gobarar ta tashi a babbar kasuwar Litinin ta Maiduguri, inda ta lalata shaguna da kayayyaki na biliyoyin Naira.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
