News
Gobara ta kone sansanin ‘yan gudun hijira a jihar Borno
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
An samu a sarar dukiyoyi da wasu kayayyaki masu daraja a wata gobara da ta tashi a wani sansanin ‘yan gudun hijira da ke Muna a karamar hukumar Jere a jihar Borno.
Jaridar Daily Post ta ruwaito cewa gobarar ta tashi ne da sanyin safiyar Laraba.
Mutane 4 sun mutu yayin daa wata babbar mota dauke da kwantena ta murkushe Motoci uku
Jami’an Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno (SEMA), sun kai ziyarar tantance wuraren da lamarin ya faru.
Har zuwa lokacin cika wannan rahoto, ba a tantance musabbabin tashin gobarar ba.
Wannan na zuwa ne kwanaki kadan bayan wata gobara ta kone shaguna da dukiyoyi na miliyoyin Naira a babbar kasuwar Gamboru da ke Maiduguri babban birnin jihar Borno.
Advertisements
