Connect with us

News

Majalisar wakilai Za ta Karfafawa Hukumomin Tsaro don Tunkarar Kalubalen Tsaro — Abbas

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Kakakin Majalisar Wakilai Tajudeen Abbas ya ce majalisa ta 10 za ta yi kokarin karfafa rundunar sojojin Najeriya da sauran hukumomin tsaro domin tunkarar kalubalen tsaro a Najeriya

Kakakin majalisar ya bayyana hakan ne a wani taron kwanaki biyu bayan rantsar da mambobin kwamitin tsaro na majalisar

Gwamnatin Tarayya Za Ta Kirkiro Hukumar Kula Da Filaye

Majalisa wakilai ta 10 za ta ci gaba da tallafawa kokarin hukumomin tsaro ta hanyar samar isassun kudade, samar da kayan aiki na zamani da sauransu

 

Advertisement

Kakakin Majalisar Wakilai Tajudeen Abbas ya ce majalisa ta 10 za ta yi kokarin karfafa rundunar sojojin Najeriya da sauran hukumomin tsaro domin tunkarar kalubalen tsaro a kasar.

Abbas, wanda ya bayyana hakan a wani taron kwanaki biyu bayan rantsar da mambobin kwamitin tsaro na majalisar, ya yi kira da a hada karfi da karfe domin tunkarar kalubalen tsaro masu sarkakiya a kasar.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Mista Musa Krishi, babban mai baiwa shugaban majalisar shawara kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a ya fitar a Abuja ranar Asabar.

Ya bayar da shawarar samar da cikakken tsarin tsaro na kasa, inda ya kara da cewa akwai bukatar a kara karfin rundunar soji da sauran hukumomin tsaro.

Abbas ya ce majalisar wakilai ta 10 za ta ci gaba da tallafawa kokarin hukumomin tsaro ta hanyar samar da isassun kudade, samar da kayan aiki na zamani, horaswa da inganta jin dadin jami’an tsaro.

A wani labarin kuma Gwamnatin Tarayya Za Ta Kirkiro Hukumar Kula Da Filaye

Advertisement

Rahotonni na cewa an kai wa wata makarantar Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) hari a arewacin Birnin Gaza, inda aka kashe mutane da dama tare da jikkata wasu.

Ma’aikatar lafiya da ke Zirin Gaza ta faɗa wa kamfanin labarai na AFP cewa an kashe aƙalla mutum 50 sakamakon harin da Isra’ila ta kai kan makarantar ta Al-Fakhoura da ke cikin sansanin Jabalia.

Sai dai rundunar sojin Isra’ila ta ce tana bincike kan lamarin.

BBC ba ta iya tabbatar da abin da ya faru ba, amma mun ga wani sahihin bidiyo da ke nuna mutane da yawa da aka ji wa rauni a wurin.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending