Connect with us

News

Sojoji Sun Kwato Mutane 6 Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Jihar  Kebbi

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Dakarun Bataliya ta daya Barikin Dukku da na ‘yan banga a jihar kebbi sun yi nasarar kubutar da wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su tare da fatattakar ‘yan bindiga da dama a dajin karamar hukumar Shanga da ke Jihar Kebbi.

Nasarar da aka samu ta biyo bayan wani aikin ceto da rundunar hadin gwiwa da jami’an tsaro suka yi a dajin karamar hukumar Shanga bayan rahoton wadanda aka yi garkuwa da su.

An fasa gidan yari tare da sakin fursunoni a Kasar Saliyo

A cewar daraktan tsaro, AbdulRahman Usman, maza shidan da aka ceto duk sun kasance cikin koshin lafiya da kuma walwala da jin dadi kuma an mayar da su cikin iyalansu.

Ya bayyana cewa dakarun Bataliya ta 1 na Dukku Barrack da ke Birinin Kebbi tare da hadin gwiwar ‘yan banga na yankin sun kai wani samame a tsaunin Kogon Damisa da ke kusa da Saminaka a karamar hukumar Shanga, wani gari mai iyaka tsakanin Kebbi da Jihar Neja.

Advertisement

A cewarsa, a yayin samamen, rundunar ta fatattaki ‘yan bindiga da dama tare da ceto mutane 6 da aka yi garkuwa da su.

An sanar da jami’an tsaro a yankin da suka hada da sojoji da ‘yan banga inda suka shiga cikin dajin Shanga, an yi nasarar ceto wadanda harin ya rutsa da su.

Daily Post 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending