News
Tawagar Lauyoyi Masu Zaman Kansu Kimanin 200 Sun Kudiri Aniyar Taimakawa Abba Gida Gida A Kotun Ƙoli
DAGA MUSLIM YUNUS ABDULLAHI
Kimanin Lauyoyi 200 ne masu zaman kansu daga jihohin Arewa 19 suka sadaukar da kansu Domin taimakawa Gwamna Kabir Yusuf na jihar Kano don samun nasara a ƙarar da ya shigar a Gaban Kotun Ƙolin Najeriya.
Yan sanda sun kama hadimin gwamnan Kano bisa zargin karkartar da tallafin kayan abinci
Da yake jawabi ga manema labarai a Arewa House, A Yau Lahadi a Kaduna, Mai magana da yawun lauyoyin, Yusuf Ibrahim, ya bukaci shugaban kasa Bola Tinubu da kotun koli da kada su bari Najeriya ta zama kasa mai jam’iyya ɗaya, Yana mai cewa al’ada ce ta dimokuradiyya mara kyau.
Lauyoyin sun dage cewa dole ne a bi doka don tabbatar da kuri’un kowane dan Najeriya a lokacin zabe.
Sun kuma bayyana goyon bayansu ga Abba K Yusuf yayin da suke bayyana cewa hukuncin da Kotun Ɗaukaka Kara ta yanke babu adalci a cikinsa
-
News2 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News7 days ago
2027: INEC Ta Tabbatar Da Ibrahim Ali Amin Little A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano A Jam’iyyar ADC
-
News5 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
