Connect with us

News

Zargin damfarar dala biliyan 2.3: ‘A shirye nake in bayar da shaida a kotu -Obasanjo

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa a shirye yake ya bayar da shaida ga Najeriya game da tsohon ministan wutar lantarki da karafa, Olu Agunloye a kan dala biliyan 2.3 da ake takaddama a kai kan kwangilar samar da wutar lantarki ta Mambilla.

Kamfanin Sunrise Power da Najeriya sun yi takun-saka a cibiyar kasuwanci ta kasa da kasa da ke ICC da ke birnin Paris na kasar Faransa, yayin da kamfanin ke zargin karya kwangilar.

Da hannun wasu ‘manyan ƙasa’ cikin ɗaukar nauyin ‘yan ta’adda a Nijeriya -Minista

Sunrise Power ta ce gwamnatin tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ce ta ba ta kwangilar ginawa, gudanar da aiki da kuma canja wurin dala biliyan 6 a watan Mayun 2003.

Kamfanin dai na zargin gwamnatin tarayyar Najeriya ta yi watsi da yarjejeniya tare da neman a biya ta dala biliyan 2.3.

Advertisement

Kamfanin ya kara da cewa tuni ya kashe miliyoyin daloli kan masu ba da shawara kan harkokin kudi da shari’a kafin a yi watsi da kwangilar.

Sai dai a nata bangaren gwamnatin Najeriyar na zargin zamba da almundahana da jami’an gwamnati wajen bayar da kwangilar.

A cikin wasikar da ya aike wa babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a Lateef Fagbemi, lauyan gwamnatin Najeriya, tsohon shugaban kasar ya bayyana aniyarsa ta bayar da shaida a madadin gwamnatin Najeriya “ta kowace fuska.

 

 

NEWS POINT NIGERIA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending