News
Ɓarauniyar Yara Ta Shiga Hannun Ƴan Banga A Jihar Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Jami’an hukumar ƴan banga a jihar Kano sun cafke wata mata da ake zargi da satar yara a unguwar Sharaɗa da ke ƙaramar hukumar Gwale.
Wikki Times ta ruwaito cewa Kwamandan ƴan bangan, Shehu Rabi’u, ya bayyana cewa matar tana saida yara kan kuɗi Naira Miliyan Ɗaya maza mata kuma N800,000.
Ya ce jami’an sun farga da matar ne a lokacin da ta ke ƙoƙarin yaudarar wata mata mai ƴaƴan huɗu: maza biyu mata biyu, inda take cewa uwar za ta kai yaran wani gida inda za a ba su kuɗi da kayan abinci.
Ya ci gaba da cewa, “Bayan mun yi kwanton ɓauna mun yi nasarar damƙe matar tare da mika ta da yaran ga ƴan sanda
Advertisements
