News
Gwamnan Jihar Ondo Ya Sauke Kwamishinonin Jihar Baki Ɗaya
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Sabon Gwamnan Jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa ya dakatar da dukkanin Kwamishinonin jihar baki daya nan take.
Hakan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da sakataren yada labaransa, Prince Ebenezer Adeniyan, ya fitar a ranar Laraba.
Abin da ya sa Hisbah take neman fitattun yan Tiktok shida a jihar Kano
Sanarwar ta umarci dukkanin Kwamishinonin da manyan sakatarori gwamnatin jihar da su sauka kan mukamansu nan take.
Sanarwar ta kara da cewa gwamnan ya kuma umarci dukkanin masu bai wa tsohon gwamnan da ya rasu, marigayi Rotimi Akeredolu shawara da su ajiye mukamansu.
A watan da ya gabata ne Leadership ta ruwaito yadda gwamnan ya rasu bayan fama da rashin lafiya.
Advertisements
