News
Rikicin Siyasar Jihar Ondo Na Kara Daukar Sabon Salo
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Magoya bayan mataimakin gwamnan jihar Ondo, Hon Lucky Aiyedatiwa da na gwamnan jihar, Rotimi Akeredolu, na shirin gudanar da wata gagarumar zanga-zanga a Akure, babban birnin jihar Ondo, a cikin makon nan.
Magoya bayan mataimakin gwamnan sun sanar da shirye-shiryen zanga-zangar a shafukan sada zumunta daban-daban a karshen mako, kamar yadda magoya bayan Akeredolu suma suka sha alwashin gudanar da zanga-zangar adawa.
Idan Za’a Sake Zaben Zamfara Sau 100 Sai Na Lashe — Gwamna Dauda
Dan majalisar wakilai Kokade Akinjo ne ke jagorantar zanga-zangar adawa da Akeredolu.
Sai dai , wata kungiya a jihar am ta yi kira ga magoya bayan gwamnan da mataimakinsa da su maida takubansu cikin kube domin tabbatar da zaman lafiya a jihar.
A wani labarin kuma Idan Za’a Sake Zaben Zamfara Sau 100 Sai Na Lashe — Gwamna Dauda
Sojojin Isra’ila sun ce sun yi wa birnin Jabalia da ke arewacin Gaza ƙawanya, inda ta ce dakarunta sun shirya ɗaukar mataki na gaba.
Jabalia na a arewacin birnin Gaza, wanda ya fuskanci kazamin faɗace-faɗace tun soma yaƙin.
A wata sanarwa sa’o’i kaɗan da suka wuce, dakarun tsaron Isra’ila sun ce sun kai hare-hare kan shingayen Hamas 250 a ranar Litinin ta hanyar amfani da jiragen yaƙi da ake sarrafasu.
Wannan ya kunshi hanyoyin karkashin ƙasa guda uku a yankin Jabalia, inda suka kashe gomman mayaka, a cewar dakarun Isra’ilar.
Sai dai BBC ba ta iya tabbatar da wannan iƙirari na dakarun tsaron Isra’ilar ba nan take.
