News
Wasu Fasinjojin Jirgi Sun Gudanar Da Zanga – zanga Kan Jinkirta Tashin Jirgi A Jihar Kano
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wasu fasinjojin jirgi da suka fusata a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano MAKIA, da ke jihar Kano, sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da tsaikon da jirgin Max Air ya yi a yayin da suke shirin zuwa Legas.
Jirgin na kamfanin Max Air mai lamba (VM1645) wanda aka shirya zai tashi da farko da karfe 1:00 na rana, sai aka jinkirta lokacin tashisa shi ba tare da an sanar da fasinjojin ba, inda suka zauna na kusan sa’o’i biyar.
Hukumar INEC ta kashe Naira biliyan 313.4 wajen shirya zaɓen Shakarar 2023 – Rahoto
Bayanai sun yi nuni da rashin isar da sako daga kamfanin ya kara dagula lamarin, wanda ya haifar da tashin hankali a bangaren sufurin cikin gida.
Daily Trust ta ruwaito cewa Malam Abubakar Muhammad wanda yana cikin fasinjojin da abin ya shafa, ya ce ya kamata ya je Legas domin a duba lafiyarsa.
