Connect with us

News

Gwamnatin Jihar Kano Ta Haramta Dukkan Fina-finan Dake Nuna Fadan Daba Da Harkar Daudu A Fadin Jahar

Published

on

Advertisements
ads

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Biyo bayan korafe-korafen da al’umma keyi a kan shirya fina-finan dake nuna fadan Daba da harkar Daudu a jahar Kano. Shugaban Hukumar tace fina-finai da Dab’i ta jahar Kano Abba El-mustapha ya bada umarnin dakatarwa tare da hana dukkan fina-finan dake nuna fadan daba da harkar daudu a fadin jahar Kano.

Abba El-mustapha na bada wannan umarni ne a yau jim kadan bayan wata ganawa da yayi da manyan ma’aikatan Hukumar tace fina-finan na Kano tare da wasu daga cikin wakilan yan masana’antar shirya fina-finan ta kannywood wanda suka hada da kungiyoyin MOPPAN, AREWA FILMS MAKERS DIRECTORS da kuma PRODUCERS.

Hakan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na ma’aikatar tace Fina-Finai Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar

Hukumar JAMB Ta Sake Tsawaita Lokacin Rajistar Neman Gurbin Karatu Na DE

Haka zalika Abba ya kara da cewa doka ce ta bawa Hukumar damar dakatarwa ko hana duk wani film da take ganin yaci karo da tarbiya tare da al’adar al’ummar dake jahar, a saboda haka tuni lokaci ya shige da za’a saka ido irin wannan gurbatattun fina-finai su cigaba da yaduwa a cikin al’umma.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending