News
Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Wakilin Gidan Talabijin Na Channels
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wani dan jarida kuma wakilin gidan talabijin na Channels, Joshua Rogers, a gidansa da ke Rumuosi a karamar hukumar Obio/Akpor ta jihar Ribas a daren jiya Alhamis.
Rogers wanda ke aiki a gidan gwamnatin jihar Ribas, rahotanni sun ce an bi sawun sa ne bayan ya fito daga aiki zuwa gidansa.
Duk Da Tsadar Wutar Lantarki An Gaza Wadata ‘Yan Najeriya Da Hasken Wutar
Barayin sun tare shi kafin ya sauko daga motarsa, inda suka nuna masa bindiga da misalin karfe tara na dare. Wata majiya da ta nemi a sakaya sunanata ta ce tun da farko dan jaridar ya ba da labarin wani taron da aka yi a Ndoni a karamar hukumar Ogba-Egbema-Ndoni na jihar inda Gwamna Siminalayi Fubara, ya kaddamar da wata cibiyar kula da lafiya a matakin farko.
-
News7 days ago
Gwamnatin Kano Ta Umarci Masu Talla Da Masu Sana’ar Jari Bola Su Bar Karkashin Gadar Tal’udu
-
News3 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News3 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
