Connect with us

News

Da Dumi Dumi: Kotu Ta Tabbatar Da Dakatarwar Da Aka Yi Wa Ganduje Daga  Shugaban Jam’iyyar APC

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Babbar Kotun Jihar Kano ta tabbatar da dakatarwar da aka yi wa Shugaban Jam’iyyar APC na Kasa, Dokta Abdullahi Umar Ganduje, daga jam’iyyar.

An dai dakatar da tsohon gwamnan Kano, Ganduje, daga Jam’iyyar APC ne a mazabarsa, kan zargin rashawa.

Cutar Zazzabi Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutune 45 A Kauyen Jihar Kano

A ranar Litinin ne dai shugabancin jam’iyyar na mazabar Ganduje suka sanar da dakatar da shi.

Amma daga bisani wani sashi na shugabancin jam’iyyar an kuma na jiha ya sanar da korar wadanda suka sanar da dakatar da Gandujen.

Kotun dai ta dage sauraron karar zuwa ranar 30 ga watan Afrilu, 2024.

Advertisement

Wannan dai na zuwa ne a ranar da hukumar yaki da rashawa ta jihar Kano ke sa ran gufanar da Ganduje da gaban kuliya kan zargin almundahana a zamanin mulkinsa a jihar.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending