Connect with us

News

Gwamnatin  Shugaba Tinubu za ta sake duba yadda gwamnatin Buhari ta jinginar da filayen jiragen sama biyu

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, ya bayyana cewa Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu za a sake bibiyar kwangilar jinginar da Filayen jiragen sama guda biyu, wanda gwamnatin Buhari ta yi.

Advertisement

Keyamo ya bayyana haka a Abuja, a taron Majalisar Zartaswa ta Ƙasa.

Majalisar Dattawa Ta Fara Yunkurin Ragewa Karfin Fada Ajin Da CBN Ke Da Shi

“Za mu sake ko sabunta kwangilar jinginar da filayen jiragen biyu, domin a fito da komai a yi komai keƙe-da-ƙeƙe.

Advertisement

Ya ce har yanzu haka an dakatar da batun kafa Nigerian Air.

Ya ƙara da cewa Jirgin Kamfanin Ethiopian Airlines ne tsohon Ministan Hadi Sirika ya shafa wa fenti da tutar Najeriya, ya ƙaddamar da shi.

Advertisement

“Tilas Nigerian Air ya zama na cikin gida kacokan”, inji Keyamo.

Cikin shekarar da ta gabata ne tsohon Ministan Harkokin Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika ya yi gidogar ƙaddamar da Nigerian Air, Kwanaki biyu kafin ya sauka daga minista.

Advertisement

Premium Times ta ruwaito cewa Kwanan nan Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da belin sa da na ‘yar sa, bayan an damƙe shi ana neman Naira biliyan kusan 20 a hannun sa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending