Connect with us

News

Kotu Ta Daure Wani Manomi Da Ya Yi Wa  Tsohuwa Mai Shekaru 65 Fyaɗe

Published

on

DAGA YASIR KABIRU BASIRU 

Kotun majistare dake Ado-Ekiti a jihar Ekiti ta daure wani manomi mai shekaru 45 Abajigbin Gbenga a gidan gyaran hali.

Alkalin kotun Dolamu Babalogbon wanda ya yi watsi da rokon sassauci da Gbenga ya nema ya yanke wannan hukunci ne bayan an same shi da laifin yi wa mata mai shekaru 65 fyade.

Ka Guji Maimaita Kuskuren Da Buhari Ya yi Na Son Zuciya  – Shehu Sani Ya  Gargadi Tinubu

Dan sandan da ya shigar da kara Sodiq Adeniyi ya ce Gbenga ya aikata wannan ta’asa a watan Afrilun 2024 a Ipole Iloro- Ekiti.

Adeniyi ya ce matan ta kira Gbenga domin ya yi mata feshi a gonanta.

“ A wannan rana da ya kamata Gbenga ya je ya yi aikin feshin sai ya roki matan ta kawo masa maganin feshin gida ya haɗa daga nan sai su garzaya ginar.

Advertisement

Ko da ta kawo masa maganin sai ya danneta ya yi lalata da ita.

Babalogbonya ce Gbenga zai zauna a gidan gyara hali har sai kotu ta kammala yin shawara da fannin dake gurfanar da masu aikata laifi irin haka na jihar.

Premium Times ta rawaito cewa za a ci gaba da shari’a ranar 31 ga Yuli.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending