Connect with us

News

Tankar Dakon Mai Kife Tare Da Kamawa Da Wuta A Kano

Published

on

Tankar Dakon Mai Kife Tare Da Kamawa Da Wuta A Kano

DAGA  SANI ABDULLAHI TUKUNTAWA

Wata tankar dakon mai ta kife kuma ta kama wuta a kauyen Tsaida da ke kan hanyar Gaya zuwa Dutse a karamar hukumar Gaya a dake Kano.

Rahotanni na nuni da cewa ba a sami rahoton asarar rai ba.

Shugaba Tinubu Ya Bayyana Goyon Bayansa Na Samar Da Halastacciyar Ƙasar Falasɗinu

Hakimin Kauyen na Tsaida, Aliyu Adamu, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sakon murya, inda ya bayyana cewa tankar ta fadi da sanyin safiyar ranar, duk da cewa har yanzu ba a san musabbabin hadarin ba.

Haka zalika Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da faduwar wata tankar dakon Mai tare da kamawa da wuta a yankin Tsaida da ke karamar hukumar Gaya.

Al’amarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11 na wannan rana, kamar yadda mai magana da yawun hukumar Saminu Yusif Abdullahi ya tabbatar wa Dala FM.

Advertisement

Ya ce, tuni aka tura jami’an kwana-kwana daga ƙaramar hukumar Wudil, domin kai ɗaukin gaggawa.

 

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending