Connect with us

News

Sarkin Kano Muhammad Sunusi Ya Fito Domin Jagorantar Zaman Fada

Published

on

Sarkin Kano Muhammad Sunusi Ya Fito Domin Jagorantar Zaman Fada

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Sarkin Kano Malam Muhammad Sanusi II ya fito domin fara jagorantar zaman fada na Yau Juma’a a fadar Sarki da ke Kofar Kudu.

Advertisement

Wanann na zuwa ne bayan jami’an tsaro sun mamaye gidan Sarkin Kano, tare da hana Sarki Muhammadu Sunusi fita don tafiya masarautar Bichi.

DA ƊUMI-ƊUMI: Jami’an Tsaro Sun Mamaye Fadar Sarkin Kano Sun Hana Shiga Ko Fita

Da fari Sarki Sanusi ya shirya jagorantar tawaga zuwa raka sabon hakimin Bichi zuwa fadarsa, tare da gudanar da wasu aika-aikace.

Advertisement

To amma tuni dubban jamian tsaro suka mamaye fadar Sarki ta Kofar Kudu don hana Sarkin Fita zuwa ziyarar da ya shirya gudanarwa.

Kawo yanzu haka Sarkin ya zauna domin fara jagorantar zaman fada na Yau Juma’a kamar yadda ya saba gudanarwa.

Advertisement

PREMIER RADIYO ta ruwaito cewa babu tabbacin suwa ne suka bayar da umarnin girke jamian tsaro a fadar Sarki da ke Kofar Kudu, amma zargi na alamta bangaren masu hamayya da gwamnatin Kano ne ke da hannu kan batun.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending