News
Gwamnan Kaduna Ya Mayarwa Iyalan Abacha Filayen Da El Rufai Ya Kwace
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnan Kaduna Uba Sani ya mayar wa iyalan tsohon shugaban kasa Janar Sani Abacha filayen su guda 2 da tsohon gwamna Nasir El Rufai ya kwace a lokacin mulkinsa.
Daily Trust ta ruwaito cewar lauyan iyalan tsohon shugaban kasar Reuben Atabo ne ya bayyana haka ga manema labarai.
Ademola Lookman Ya Lashe Kambun Gwarzon Dan Kwallon Afirka Na 2024,
Sanarwar gwamnatin jihar Kaduna da Babban Daraktar ma’aikatar kula da filaye Mustapha Haruna ya gabatar tace Gwamna Sani ya rubutawa iyalan Janar Abacha wasika wanda aka sanya sunan Mohammed Sani Abacha da ta bayyana mayar musu da filayen da kuma gabatar musu da bukatar cewar su je su biya harajin da aka saba karba a hannun su na mallakar filayen.
A shekarar 2022 tsohon gwamnan jihar El Rufai ya gabatar da sanarwa a jarida a ranar 28 ga watan Afrilu wadda ta bayyana kwace filayen tare da soke takardun wadanda aka mallakawa.
Wannan mataki na tsohon gwamnan ya haifar da cece kuce sosai a ciki da wajen jihar Kaduna.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
