Connect with us

Sports

Ademola Lookman Ya Lashe Kambun Gwarzon Dan Kwallon Afirka Na 2024,

Published

on

Ademola Lookman ya lashe gwarzon dan wasan kwallon kafa na Afrika da CAF ke bayarwa
Spread the love

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

Ademola Lookman ya lashe kambun gwarzon dan kwallon Afirka na 2024, inda ya doke ‘yan wasa kamar su Adingra, Guirassy, Hakimi, da Inaki Williams.

Advertisement

Jajircewar Lookman a kungiyar Atalanta a gasar Serie A, da rawar da ya taka wajen taimaka wa kungiyar da kuma gudummawar da ya bai wa tawagar Najeriya, suka sa ya zama wanda ya fi kowa cancanta wajen lashe wannan kyauta.

Rundunar Sojoji Ta Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindigar Da Ya Kashe Sarkin Gobir

Lookman ya bayyana jin dadinsa na lashe kyautar ta wannan shekarar, kuma masoyansa sun bayyana jin dadinsu yadda ya ci kwallaye da kuma taimaka wa kungiyarsa.

A lokacin karbar kyautar, Lookman ya gode wa ‘yan wasan tawagarsa, masu horaswa, da iyalinsa, wajen taimaka masa.

Advertisement

“Wannan kyauta ta cika min burina, kuma ina fatan hakan zai zaburar da matasa daga Afirka su yarda da kansu.

“Wannan nasara tana nuna aikin tukuru da sadaukarwa da na yi.”

Wannan nasara ta kara tabbatar da matsayin Lookman a matsayin daya daga cikin taurarin Afirka masu haskawa.

Advertisement

Magoya baya daga fadin nahiyar Afirka sun yi murna da wannan nasara, inda Lookman ya shiga cikin jerin manyan ‘yan wasan Afirka da suka lashe wannan kyauta.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *