Connect with us

News

Gwamnan Kano Ya Amince Da Murabus Din Kwamishinan Ma’aikatar Bibiya Da Tabbatar Da Nagartar Aiki

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da murabus din kwamishinan ma’aikatar bibiya da tabbatar da nagartar aiki Injiniya Mahammad Diggol.

Advertisement

Bayanin hakan na kunshe a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar.

DA DUMI-DUMI:  Kwamishina Ya Yi Murabus A Kano

An dai nada Muhammad Diggol a matsayin kwamishinan sufuri a farkon gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf a shekarar 2023.

Advertisement

Daga baya gwamnan ya mayar da shi ma’aikatar bibiya da tabbatar da nagartar ayyuka, inda ya yi aiki har zuwa wannan lokaci da ya yi murabus.

Gwamna Yusuf ya bayyana godiyarsa ga Engr. Diggol bisa hidimarsa da jajircewa gami da sadaukarwar da ya yi a lokacin da yake matsayin dan majalisar zartarwa ta jiha.

Advertisement

A cewar sanarwar, Gwamnan ya kuma mika sakon fatan alheri ga Engr. Diggol a cikin al’amuran rayuwarsa ta gaba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending