Connect with us

News

DA DUMI-DUMI:Gwamnan Kano Ya Rantsar Da Sabbin Kwamishinoni Guda  7

Published

on

Gwamnan Kano ya rantsar da sabbin kwamishinoni 7

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya jagoranci rantsar da sabbin kwamishinoni guda bakwai da ya nada a watan Disambar 2024 da ya gabata.

Advertisement

Kwamishinan shari’a na Kano Kuma babban lauyan jihar, Barista Haruna Isa Dederi shine ya rantsar da sabbin kwamishinonin 7 tare da sauran masu baiwa gwamna shawara.

WAEC Ta Sanar Da Sabon Tsarin Gyara Jarrabawar Da Mutum Ya Fadi Ba Sai Ya Yi Jiran Shekara Daya Ba

Bugu da kari gwamnan ya jagoranci rantsar da sabbin manyan sakatarorin gwamnati guda 6 (Permanent secretaries) da aka daga likkafarsu zuwa mataki na gaba a aikin gwamnati.

Advertisement

Haka kuma gwamna Yusuf ya jagoranci rantsar da masu bashi shawara guda 13 daga cikin guda 15 da aka nada.

Rahotanni na nuni da cewa tuni gwamna Yusuf ya tura sabbin kwamishinonin zuwa ma’aikatun da aka tanadar musu.

Advertisement

Gwamnan ya amince da hakan ne a fadar gwamnatin jihar Kano ranar litinin 6 ga watan Janairun shekarar 2025.

Sabbin Kwamishinonin da gwamna Yusuf ya jagoranci rantsarwa kuma ya amince da basu ma’aikatun da zasu jagoranta sun hada da :

Advertisement

1.Alhaji Shehu Wada Sagagi, da zai kula da ma’aikatar kasuwanci da zuba jari ta kano

 

Advertisement

2.Kwamared Ibrahim Abdullahi Waya, an turashi ma’aikatar kula da yada Labarai ta Kano

 

Advertisement

3.Dr.Dahir Muhammad Hashim an amince ya rike ma’aikatar kula da Muhalli ta kano

 

Advertisement

4.Abdulkadir Abdussalam, gwamna ya amince ya rike ma’aikatar kula da Raya karkara ta Kano

 

Advertisement

5.Dr. Isma’ila Aliyu Dan Maraya ,an turashi ma’aikatar kula da Kudi ta Kano.

 

Advertisement

6.Dr.Gaddafi Sani Yakubu ,an turashi ma’aikatar Kula da makamashi ta Kano

 

Advertisement

7.Dr.Nura Iro Ma’aji , ma’aikatar gwamna Abba ya amince ya rike ma’aikatar Kula da yadda bada kwangiloli da bibiyar ayyukan gwamnati

 

Advertisement

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ce ya dauki matakin samar da sabbin kwamishinonin ne domin inganta ayyukan gwamnati da Kuma kawo cigaba a Kano.

 

Advertisement

Sabbin Kwamishinonin zasu fara zaman majalisar zartaswa na nan gaba da za’a sanar.

 

Advertisement

TST Hausa ta gano cewa a ranar Talata 18 ga watan Disamba na shekarar 2024 data gabata ne majalisar dokokin Kano ta amince da mutane 7 din da gwamna Abba Yusuf ya tura mata dan a tantancesu a kuma amince masa ya nada su kwamishinoni,bayan garambawul da yayi a cikin majalisar zartaswarsa.

 

Advertisement

Gwamna Yusuf ya taya kwamishinonin murna tare bukatarsu da su jajirce wajen gudanar da ayyukansu yadda ya kamata, tare da rungumar kowa a gwamnati dan amfana da romon Demokaradiyya.

Gwamnan ya kuma nemi sabbin kwamishinonin da masu bashi sharawa da su rike gaskiya da amana yana mai shaida cewa rantsuwar da sukayi na yiwa jama’a aiki ,rantsuwa ce ta kare muradun mutanan kano.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending